Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali- Ceto Kananan Yaran Da Aka Sace A Kano, Okotoba, 28, 2019


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Batun cin zarafin kananan yara ya ci gaba da bayyana a Najeriya inda a cikin makonni uku aka ceto kusan mutane dubu daya da suka hada da mata da kananan yara, wadanda ko dai aka sace, ko kuma aka gasawa akuba a wuraren da ya kamata a taimaka masu su iya zama 'yan kasa na kwarai.

Daga cikin wannan adadin akwai yara tara 'yan asalin jihar Kano da aka ceto a jihar Anambra inda wadansun su suka shafe kusan shekaru uku a wajen wadanda suke rike da su, wandanda suka sake masu sunaye da addininsu.

Ko a shekarun baya, an sami irin wannan rahoto inda wadansu daga kudu suka yi zargin an sace 'yarsu aka kaita arewacin Najeriya inda ita ma aka canza mata suna da addini, lamarin da ke daukar hankalin al'umma a ciki da wajen Najeriya.

Saurari cikakken shirin.

Kwato kananan yaran da aka sace a Kano-!0:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:22 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG