Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali, Mayu 24, 2018: Tashin Hankali A Tsakanin Iyali, Kashi Na Biyu


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

Makon jiya muka fara nazari kan yanayin da aka shiga inda ake kara samun ma’aurata suna kuntatawa abokan zamansu da ya shiga kaiwa ga kisa, akasin abinda aka saba gani a lokutan baya. Ta haka shirin Domin Iyali ya gayyaci masana da majibantan wannan lamarin domin neman gano masababin lamarin da kuma matakan shawo kanshi.

A yau ma muna tare da bakin namu, Barrister Maryam Ahmed wata lauya kuma ‘yar gwaggwarmayar kare hakin iyali, da Mallam Abba Bello, jami’in Kungiyar dake aikace aikacen kiwon lafiyar iyali, da kuma Dr, Haruna Yakubu na sashen kula da lafiyar kwakwalwa a asibitin koyarwa na Aminu Kano duka a birnin Kano.


Jagoran wannan tattaunawa wakilinmu Mahmud Ibrahim Kwari ya tambayi Dr Haruna Yakubu ko wannan lamarin yana da nasaba da canfin da wadansu ke yi cewa shafar aljannu ne, ko tabun hankali, kasancewa lamarin ya shafi talakawa da attajirai, masu ilimi da kuma marasa ilimin Boko.

Saurari cikakken bayanin nasa da na sauran kwararru a shirin na yau.

Tashin Hankali A Tsakanin Iyali, Kashi Na Biyu-10:20"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:20 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG