Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU, Domin Iyali: Satumba 21, 2017- Hira da Frederica Wilson


Yar majalisar dokokin Amurka Frederica Wilson da Grace Alheri Abdu
Yar majalisar dokokin Amurka Frederica Wilson da Grace Alheri Abdu

Makon da ya gabata gwamnatin tarayyar Najeriya tayi bukin sallamar ‘yammatan Sakandaren Chibok dari da shida da kungiyar Boko Haram ta saki bayan garkuwa dasu na tsawon shekaru uku. Gwamnatin tarayya ta ajiye ‘yammatan a wata cibiya dake birnin tarayya Abuja domin kula da lafiyarsu da kuma taimakonsu su iya fuskanta rayuwar yau da kullum. Kafin gudanar da wannan bukin wata tawagar ‘yan majalisar dokokin tarayyar Amurka karkashin jagorancin Frederica Wilson sun kai ziyarar gani da ido a Najeriya. Bayan dawowarsu kuma nayi hira da ‘yar Majalisa Frederica wadda ta fara da bayyana makasudin zuwanta Najeriya.

Hira da Frederica Wilson-10:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:35 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG