Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnan Jihar Ekiti Fayose ya bukaci gwamnatin Tarayya ta sasanta ‘yan Arewa da kabilar Igbo


Shugaba Buhari da mataimakinsa Osibanjo

Gwamna Ayodele Fayoshe yace lamarin abin takaici ne, bashi cikin ra’ayin kasar mu irin haka ya rika faruwa. Yace idan aka duba za’a ga cewa kasar Nigeria tafi rarrabuwa a cikin shekaru biyu da suka wuce, kuma wannan ba shine shugabanni irin su marigayi Tafawa Balewa da Dokta Nnamdi Azikiwe da Cif Obafemi Awolowo suke son gani ba.

A kan batun ballewar kabilar Igbo daga Najeriya, Gwamna Fayoshe yace wannan ba ra’ayin shugabanni mu na farko bane, amma ina son gwamnatin tarayya ta zama uba ga kowa, a saurare kowa a yi sulhu, saboda sulhu itace hanya mafi kyau na shawo kan kowa ce matsala. Zaman dardar ya yi yawa a Najeriya, ya kamata a zauna da al’umman Igbo a tattauna da su.

Da ya ci gaba da bayani, Gwamnar na jihar Ekiti yace yana nufin Najeriya ta kasance kasa daya. Yace ko a turai ana samun irin wadannan matsaloli, yayi misali da Northern Ireland da Britaniya, amma hanyar magance su sune a zauna ayi sulhu.

Yace a saurari kowa, gwamnatin tarayya ta kula da kowa. Gwamna Ayodele Fayoshe yace mafita itace gwamnatin Najeriya ta canza dabi’unta, Najeriya kasa ce mai kabilu da yawa kada a yi amfani da karfi a rufe bakin wasu jama’a. Gwamnan Fayose yayi wannan furucin ne a hirarsa da wakilin sashen Hausa Hassan Umaru Tambuwal.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:31 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG