Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Kaduna Ta Ayyana Kwanaki 3 Don Jimamin Mutuwar Sarkin Zazzau


Gwamnatin jihar Kaduna ta ayyana kwanaki uku don nuna alhinin mutuwar mai Martaba Sarkin Zazzau Alhaji Shehu Idris.

Mai ba gwamnan jihar Kaduna Nasirsu El-Rufa’i shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa, Muyiwa Adeleke ne ya sanar da hakan a wata sanarwa ranar Litinin 21 ga watan Satumba.

Adeleke ya ce ma’aikatun gwamnati za su yi aiki kamar yadda ka saba a ranakun 21 da 22 ga watan Satumba, amma ranar Laraba 23 ga watan Satumba za ta zama ranar hutu don tunawa da sarkin.

A cewarsa, “za a sassauto da tutoci a ranakun makokin.”

Sarkin ya rasu ne a asibitin sojan 44 da ke jihar Kaduna ranar Lahadi 20 ga watan Satumba yana da shekaru 84 a duniya.

An yi jana’izar Sarkin a masarautarsa da ke Zaria a kusa da sarakunan masarautar na baya da suka riga mu gidan gaskiya.

Babban limamin masarautar Zazzau, Dalhatu Kasimu ne ya jagoranci sallar jana’izar a fadar masarautar Zazzau da misalin karfe 5:35 na yammacin ranar Lahadi, kuma dubban mutane ne suka halarci taron jana’izar.

Daga cikin wadanda suka halarci jana’izar harda Malam Nasir El-Rufa’i, da sakataren gwamnatin Kaduna Balarabe Lawal-Abbas, da shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna Yusuf Zailani da wasu mukarraban gwamnati, da kuma manyan sarakunan arewacin kasar.

An nada Alhaji Shehu Idris a matsayin Sarkin Zazzau a ranar 15 ga watan Fabarairu a shekarar 1975 kuma ya shafe shekaru 45 yana mukin masarautar kafin mutuwarsa.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG