Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Lebanon Ta Ayyana Dokar Ta Baci a Beirut


Wani gini da ya lalace sakamakon fashewar da ta auku
Wani gini da ya lalace sakamakon fashewar da ta auku

Gwamnatin Lebanon ta ayyana dokar ta baci ta tsawon makwanni biyu a yau Laraba a Beirut, kana ta umarci rundunar soji da ta yi daurin talala ga duk wanda ke da hannu a ajiye kayayyaki masu fashewa da suka tarwatse a tashar jiragen ruwan birnin, lamarin da ya shafi dukkan gine-ginen da ke kusa, ya kuma yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

Dokar ta baiwa rundunar sojin cikakken iko bayan mummunar fashewar da ta auku a ranar Talata.

Har yanzu ba’a kai ga gano ainihin musabbabin fashewar ba, to amma jami’an kasar ta Lebanon suna ba da karfi ne akan abin da suka ce ton-ton na sinadarin ammonium nitrate da aka adana a tashar jiragen ruwan tsawon shekaru shida.

wani mutum yana kwashe gilashin ginin wani masallaci da fashewar da ta auku ya lalata
wani mutum yana kwashe gilashin ginin wani masallaci da fashewar da ta auku ya lalata

Fashe-fashen sun lalata daukacin gine-ginen da ke kusa, suka kuma kashe akalla mutane 135, tare da jikkata fiye da wasu dubu biyar, a cewar Ministan lafiya Hamad Hassan a yau Laraba.

Gwamnan Beirut Marwan Abboud, ya ce wannan mummunan ibtila’in ya kuma raba mutane kusan dubu dari uku da gidajensu.

Ma’aikatan ceto na ci gaba da binciken wadanda lamarin ya rutsa da su a yau Laraba, a yayin da Firai Minista Hassa Diab, ya ayyana zaman makoki na kwanaki 3 a fadin kasar.

Jami’ai sun ce suna sa ran adadin wadanda lamarin ya rutsa da su ya karu, a daidai lokacin da ma’aikatan ceto ke ci gaba da binciken baraguzan gine-ginen da suka rushe, a yayin da sauran mutane ke ci gaba da neman ‘yan uwa da abokai da ba’a gani ba.

Baba Yakubu Makeri ya yi hira da Hudu Jasir Umar, wani dan asalin kasar Ghana da ke zaune inda lamari ya faru, ya kuma bayyana halin da a ke ciki.

saurari bayanin nasa.

Hira da Hudu Jasir Umar kan fashewar da ta auku a Beirut:3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:15 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG