A dai-dai lokacin da mutane ke komawa garuruwan su na asali a tarayyar Najeriya biyo bayan nasarar da aka samu da yaki da Boko Haram, gwamnatin tarayya tace zata kyautata yanayi a wadannan yankunan da wannan lamari ya shafa domin mutanen wadannan wuraren su samu natsuwa.
Mutanen dai sun jima cikin damuwa na hasarar da suka yi ta ‘yan uwansu da dukiyoyin su abinda yasa gwamnatin tace wajibi ne ta kyautata rayuwar su musammam ma wajen samar musu ababen more rayuwa.
Wannan ne yasa Mataimakin shugaban kwamitin kula da ‘yan gudun hijiran, Alhaji Tijjani Tumsa ya shaidawa wakilin muryar Amurka Nasir Adamu El-Hikaya cewa sun fara magana da masu ruwa da tsaki a harkan ilmi domin gyara makarantu a wadannan jihohin da lamarin ya shafa.
Yace kwamitin kula da komawar ‘yan gudun hijiran zai taimakawa wadannan mutanen da ganin sun sake gina gidajen su.
Ga Nasir Adamu El-Hikaya da Karin bayani 2’54:
Facebook Forum