Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Inganta Samar Da Wutar Lantarki Da Kuma Ruwa


 Muhammadu Buhari
Muhammadu Buhari

Majalisar zartaswar tarayyar Najeriya ta dauki muhimman matakan da zai kai ga inganta samar da wutar lantarki da kuma samar da wadataccen ruwan sha da na noma.

Bayanda majalisar ta kammala taronta na mako mako karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari, gwamnatin ta bada sanarwar cewa zata dauki mataki mai kwarin gaske domin tabbatar da cewa an sami inganci a fannin harkokin tsaro a kasar da kuma kare haduran sufurin sama kamar yadda yake a sauran kasashen duniya.

A fannin samar da wutar lantarki, ministan albarkatun ruwa Suleiman Adamu Kazaure ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya zata fito da wani tsari da za a kara inganta hanyoyin samar da wuta, bisa ga cewarshi, za a duba kamfanonin da ba zasu iya samar da wuta yadda ya kamata ba, sai gwamnati ta nemi hanyar da zata shiga ciki.

A nasa bangaren, ministan harkokin sufurin sama Saneta Hadi Sirika yace gwamnatia zata sayi sabuwar na’urar tantance dalilin hadura irin na zamani domin inganta harkokin sufurin jiragen sama.

Ga dai rahoton da wakilinmu Umar Faruk Musa ya aiko daga Abuja

Rahoton Kama Wadansu da nakiyoyi a Ghana-2:42"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:43 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG