Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

INDIA: Yar Shekara 17 Da Aka Yiwa Fyade Tare Da Cinna Mata Wuta Tana Asibiti Rai Hannun Allah


Gangamin kiran gwamnati ta dakile yiwa yara mata fyade a kasar India
Gangamin kiran gwamnati ta dakile yiwa yara mata fyade a kasar India

Yiwa yara mata fyade a kasar India ba sabon abu ba ne amma na wata yarinya 'yar shekaru 17 da haihuwa ya dauki wani salo inda matashin da ya yi mata fyade ya cinna mata wuta, rabin jikinta ya kone yanzu tana kwance a asibiti rai hannun Allah

Wata yarinya mai shekaru 17 da haifuwa da aka cinna mata wuta bayan an yi mata fyade a gabashin India tana kwance a asibiti rai hannun Allah, yayin da rabin jikinta ya kone a fadar jami’an kiwon lafiya.

An kaiwa wannan matashiya hari ne a ranar Juma’a, bayan fyade da aka yiwa wata yar shekaru 16 kana aka konata har lahira a cikin jiha guda wato Jharkhand.


'Yan sanda sun kama wani mutum mai shekaru 19 da suke kauye daya da yarinyar mai shekaru 17. An ce shi ne ya zuba mata kanazir kana ya cinna mata wuta yayin da taki yarda ya yi lalata da ita.


Ana zargin wasu, mutane hudu da yin garkuwa da kuma fyade da wata yarinyar mai shekaru 16 a makon da ya gabata. Bayan an wayi gari iyayen yarinyar sun kai kara ga dattijan kauyen inda aka ci mutanen tarar kudi. Jami’ai sun ce mutanen hudu sun fusata da wannan tarar dala dari bakwai da hamsin da aka dora musu, a kan haka suka cinna wuta a gidan su yarinyar yayin da take ciki domin suka kasheta.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG