Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Israila Da Falasdinawa Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta


Makarantar yara da rokar Falasdinawa ta lalata lokacin fafatawarsu

Da taimakon kasar Masar wadda ta shuga tsakani, Israila da Falasdinawa sun kulla yarjejeniyar sagaita wuta a fafatawa da suke yi akan iyakarsu da Zirin Gaza lamarin da ya sa yanzu kura ta lafa

Jiya Laraba tarzoma ta lafa akan iyakar Isira’ila da Gaza, a yayinda jami’an Palasdinawa suka ce Masar ta shiga tsakanin an kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isira’ila.

Jami’an Isira’ila basu tabbatar da kula yarjejeniyar ba, amma sun ce idan ‘yan yakin sa kai a Gaza suka daina harbawa Isira’ila rokoki, itama Isira’ila zata kawo karshen hare haren da take kaiwa yankunan Palasdinawa.

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman akan shirin samun zaman lafiya a gabas ta tsakiya, yayi gargadin cewa wannan itace tarzoma mafi muni da aka ganin tsakanin bangarorin biyu, tun rikicin shekara ta dubu biyu da goma sha hudu da aka yi tsakanin kungiyar Hamas da Isira’ila.

A yan watanin da suka shige, wakilin na Majalisar Dinkin Duniya ya sha yin kashedin cewa bangarorin biyu suna dab da fadawa cikin rikici

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG