Tsohon shugaban Majalisar Dattijai na jihar Delaware wanda kuma ya yi mulki sau bi biyu a matsayin mataimakin shugaban kasa a gwamnatin Obama, zai zama abokiin takarar Sanata Bernie Sanders na jihar Vermont da sauran 'yan takarar shugaban kasa na Democrat a cikin' yan takarar da suka gabata, duk da cewa ba a tabbatar da ko zai iya yin takarar asusun bada gudumawa ba.
Biden yana da kwarewa kan harkokin waje, da fanin shari’a da kuma harkokin cikin gida wanda ba za’a iya hada shi da sauran ‘yan takara ba.
A cikin sakonnin bidiyo da aka fitar a yau Alhamis, Biden ya ce kimar da Amurka take da shi a fadin duniya da kuma abubuwan da take da shi, na cikin hatsari.
"Na yi imani tarihi zai sake duban shekaru hudu na wannan shugaban kuma duk abin da ya runguma a cikin wannan lokaci. Amma idan muka ba Donald Trump shekaru takwas a fadar White House, har abada zai canza dabi'ar wannan kasar, da mu kan mu, kuma ba zan iya tsayawa in kallon hakan ya faru ba."
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 25, 2023
Mawakiya Yar Najeriya Ta Yi Tarihi A Bikin Bada Lambar Yabo Na Oscar
-
Janairu 13, 2023
Lisa Marie Presley, Diyar Mawaki Elvis Ta Rasu
-
Janairu 11, 2023
Ana Tsaftace Yankunan Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa A California
Facebook Forum