Iran dai ta hakikance cewa ta cimma sharuddan da aka cimmawa tsakanin ta sauran kasashen nan da suka yi yarjejeniya da ita akan batun makamashin Nuclear.
Mai Magana da yawun Ministan harkokin wajen na Iran ne Bahram Ghasenni, yace kara waadin takunkumin tamkar keta haddin yarjejeniyar da aka kulla ne.
Sai dai Ghasseni bai bayyana ainihin takaimaiman matakin da za a dauka ba.
A cikin watan da ya gabata ne dai shugaban addinin kasar Ayotollah Ali Khameni yace kara tsawaita takunkumin da Amurka ke cewa zata yi tamkar keta yarjejeniyar da aka cimmawa ne kuma ba zasu yi shiru ba wanda musu cas to zasu ce masa kule.