Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Morocco Ta Koma Kungiyar Hadin Kan Kasashen Afirka AU


Military honor guards attend a welcome ceremony of French President Emmanuel Macron at the Great Hall of the People in Beijing.
Military honor guards attend a welcome ceremony of French President Emmanuel Macron at the Great Hall of the People in Beijing.

Taron da suka soma jiya Litinin ya samu kasancewar kasar Morocco a karon farko bayan fiye da shekaru talatin da ta fice daga kungiyar saboda mallakar yakin Sahara da tayi da kungiyar bata amince mata ba kuma a wannan karon ma bata canza zani ba.

Inji masu sharhi kungiyar AU ta hadin kan kasashen Afirka, kungiya ce da yakamata ta hada kawunan kasashen a zahiri.

Kamata yayi tayi duk iyakacin kokarinta ta tabbatar da mulkin dimokradiya a duk fadin nahiyar da tabbatar da kwanciyar hankali da taimakawa kasashen su farfado da tattalin arzikinsu ta yin cudanya da juna.

Kasar Morocco da yanzu ta dawo cikin kungiyar tana da karfi a harkokin kasuwanci da siyasa da kuma taimakawa kasashe a harkokin tsaro. Zamansu a ware kamar yadda Morocco tayi ba abun da zai gyara kasashen Afirka ba ne. Saboda mahimmancinta ya sa da zara ta furta aniyyar komowa suka yi maza-maza suka karbeta.

Dangane da cewa matsalar da ta sa Morocco ta fice da can, wato batun yankin Yammacin Sahara masu sharhi na ganin yakamata a wuce wannan maganar yanzu, wadda tamkar karamar matsala ce.

Abun da shugabannin suka sa gaba shi ne abun da zasu iya kullawa talakawansu domin a samu cigaba.

Shugaban Guinea Conakry shi ne zai shugabanci kungiyar yanzu kuma ana ganin rawar da ya taka wurin warware rikicin Gambia ya sa aka amince masa. Hazakar da ya nuna cewa yana iya shiga gaba ya sa aka bashi shugabancin kungiyar.

Shi ma ministan harkokin wajen Chadi Muhammad Musa ya samu shugabancin hukumar kungiyar sanadiyar rawar da kasarsa ta taka a

harkokin tsaro, wato yaki da Boko Haram a yankin kasashen Sahel.

Ga rahoton Souley Barma da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00
Shiga Kai Tsaye


Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG