Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasashen Nijer Da Benin Za Su Gana Da Najeriya Akan Sake bude Iyakokinta


A yayinda kasashen Nijer, Benin da Najeriya ke shirin tattauna hanyoyin sake bude iyakokin Najeriya a yau Alhamis, 14 ga watan Novemba, a Abuja babban Birnin Tarayyar Najeriya, gwamnatin Jamhuriyar Nijer ta sanar cewa, matakin na hukumomin Najeriya ya haddasa gibin dubban miliyoyin CFA a asusunta sakamakon tauyewar al’amura akan iyakokin kasashen biyu.

Da yake ganawa da wata tawagar jami’an asusun bada lamuni na FMI ko IMF a ranar talatar da ta gabata, ministan kudaden kasar Nijer Mamadou Diop ya sanar cewa, matakin rufe iyakokin Najeriya ya haifar da gibi a aljihun gwamnati, a cewar sa asarar billion 40 na CFA ne wannan mataki ya janyowa kasar Nijer saboda rashin samun kudaden da aka yi hasashen zasu shiga aljihun gwamnati ta hanyar awon kaya da biyan wasu diyyoyin kan iyakar kasar da Najeriya.

Ministan kudin kasar ta Nijer ya kara da cewa tuni ma’aikatan harkokin kudade suka bullo da wasu sabbin matakai don cike wannan gibi, kafin karshen shekara yayinda a dayan gefe wasu abokan hulda suka amince zasu tallafa da gudunmowar warware wannan matsala injishi.

Dr. Soly Abdoulaye masanin tattalin arziki a Nijer ya ce, faruwar wannan al’amari wani abu ne da ya kamata ya zamewa gwamnatocin Afrika irinsu Nijer darasi.

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Nijer Kalla Hankourao a karshen taron kungiyar CEDEAO da aka gudanar a makon jiya a Yamai, ya bayyana cewa kasashen Nijer da Najeriya da Benin zasu gudanar da taro a Abuja babban Birnin Tarayyar Najeriya, domin duba hanyoyin sassauta wannan mataki da ya jefa miliyoyin talakawa cikin halin kuncin rayuwa.

Ga cikakken rahoton Wakilin muryar Amurka a yamai Souley Moumouni Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:48 0:00
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG