Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kashi 60 Zuwa 80 Na ‘Yan Kallo Za A Bari Su Shiga Kallon Wasannin Gasar AFCON Saboda COVID - CAF


Daya daga cikin filayen da za a buga gasar AFCON a Kamaru (Facebook/CAF)
Daya daga cikin filayen da za a buga gasar AFCON a Kamaru (Facebook/CAF)

A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar COVID ta sa aka dage zuwa bana.

Hukumar Kwallon Kafa ta nahiyar Afirka CAF ta ce kashi 60 zuwa 80 na ‘yan kallo za a bari su shiga filayen wasanni da za a kara gasar cin kofin nahiyar na AFCON.

Matakin a cewar hukumar na da nasaba da annobar COVID-19.

Cikin wata sanarwa da ta fitar, CAF ta ce bayan wata tattaunawa da ta yi da hukumomin cikin gida na Kamaru, sun cimma matsaya akan cewa kowanne filin wasa za a bar ‘yan kallo kashi 60 ne zuwa 80 su shiga kallo.

A ranar 9 ga watan nan na Janairu za a bude gasar ta cin kofin nahiyar Afirka, wacce Kamaru ke karbar bakunci.

Za kuma a kammala a ranar 6 ga watan Fabrairu kamar yadda jadawali gasar ya nuna.

A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar COVID ta sa aka dage zuwa bana.

Kasar Aljeriya ce ke rike da kofin gasar.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG