Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kelechi Iheanacho Ya Tsawaita Kwantiraginsa Da Leicester City


Kelechi Iheanacho
Kelechi Iheanacho

Dan wasan kungiyar kwallon kafar Leicester City, Kelechi Iheanacho ya tswaita zamansa a kungiyar da shekara uku.

Hakan na nufin dan wasan na Najeriya, zai zauna tare da jaruman filin wasa na King Power har zuwa 2024 a gasar Premier ta Ingila.

Tsawaita wannan yarjejeniya, na zuwa ne bayan da aka karrama Iheanacho da lambar yabo, saboda ya ci kwallo bakwai cikin wasa hudu da ya buga a gasa daban-daban a kasar ta Ingila.

Dan wasan ya samu lambar yabon ne a matsayin wanda ya fi fice a watan Maris a gasar ta Premier.

“Ina mai matukar farin ciki da aka ayyana ni a matsayin dan wasan da ya fi fice a watan Maris.” Iheanacho ya wallafa a shafinsa na Instagram.

Ya kara da cewa, “Ina godiya ga kungiyar Leicester, abokan wasana, manajan kungiyar, ma’aikata da duk sauran wadanda ke wannan kungiya da kuma masoyanta.”

A shekarar 2017 Iheanacho ya je kungiyar ta Leicester, ya kuma zura kwallo 32 cikin wasa 117 da ya buga mata a iya zamansa da kungiyar.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG