Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wata Kotu a Najeriya ta Daure Kabiru Sokoto Rai da Rai


Kabiru Sokoto, mutuminda ake zargi da kitsa hari kan wata majami'a a Madalla kusa da Abuja a shekara ta 2011
Kabiru Sokoto, mutuminda ake zargi da kitsa hari kan wata majami'a a Madalla kusa da Abuja a shekara ta 2011

A Najeriya wata kotun kasar ta yanke hukuncin daurin rai da rai kan Kabiru Sokoto daya daga cikin wadanda ake zargi da shirya hari kan wata maja’mi’ar darikar katholika a akuyen Abuja ranar kirsimeti a shekara ta 2011.

A Najeriya wata kotun kasar ta yanke hukuncin daurin rai da rai kan Kabiru Sokoto daya daga cikin wadanda ake zargi da shirya hari kan wata maja’mi’ar darikar katholika a akuyen Abuja ranar kirsimeti a shekara ta 2011. Kotun ta Abuja ta sami Kabiru wanda ake kira Kabiru Umar da laifin shirya wasu hare haren ta’addanci.

Kotun tace Kabiru yana da masaniya gameda shirin kungyar Boko Haram na kai hari kan maja’mi’ar St Teresa. An kashe mutane 44 a harin wasu hamsin kuma suka jikkata.

Kamar yadda kotun ta fada masu gabatar da kara sun tabatar da cewa Kabiru ya kasa ko yaki ya gayawa hukumomi cewa za a kai harin bam din.

Banda ma wannan kotun ta same shi da shirya wasu hare hare ciki harda wani da aka kai a arewacin sokoto.

Ana zargin Kabiru da zama daya daga cikin manyan jami’an kungiyar Boko Haram.Kungiyar da ake zargi da kadamar da yaki domin kafa tsarin shari’a a arewacin Najeria. Kungiyar ce ake zargi da haddasa mutuwar wasu dubban mutane tun lokacinda ta fara tada kayar baya a shekara ta 2009.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:25 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG