Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Izala Ta Yi Addu'ar Kawo Karshen Ayyukan 'Yan Ta'addanci a Najeriya


Shugaban Kungiyar JIBWIS Sheikh Abdullahi Bala Lau
Shugaban Kungiyar JIBWIS Sheikh Abdullahi Bala Lau

Mako biyu kacal gabanin azumin watan ramadna na bana hijra 1442, malamai da sauran jama'a sun taru a dakin taro na masallacin tarayya a Abuja don kaddamar da faifan karatun alkur'ani mai girma izu 60 da Imam Abbas Uzairu Chikaji Zaria ya karanta.

A wurin taro, an karfafa guiwar masu ibada su yawaita karatun don neman kariya daga miyagun iri da su ka hada da masu satar mutane da 'yan boko haram.

Masu jawabi sun karfafa cewa yanda lamuran tsaro su ka addabi jama'a musamman arewa, zai yi kyau su yi amfani da karatun alkur'ani a watan mai alfarma don neman taimakon Allah.Da ya ke jagorantar taron shugaban JIBWIS Imam Abdullahi Bala Lau ya ce dama ce ga jama'a su rika sauraron karatun ko da ba su da haddar musamman a ramadan mai shigowa don samun taimakon Allah ga fitinar da ke addabar Najeriya.

Sauran manyan malaman da su ka hakarci taron sun hada da sautus sunnah Yakubu Musa Hassan Katsina, Sheikh Khalid Jos, Dr.Abdulsalam Babangwale da sauran su.

Saurari cikakken rahoton Nasiru Adamu El-hikaya daga Abuja:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:59 0:00
XS
SM
MD
LG