Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Taliban Zata Tsagaita Wuta Lokacin Bukin Sallah


Afghanistan Eid Al Fitr
Afghanistan Eid Al Fitr

Kungiyar Taliban ta sanar yau asabar cewa zata tsagaita bude wuta kan dakarun tsaron gwamnati a duk fadin Afghanistan a cikin kwanaki uku da za a yi bukukuwan salla a karshen azumin watan Ramadan.

Tsagaita wutar ta zo daidai da bada umarnin dakatar da yunkurin murkushe kungiyar Taliban na tsawon mako guda da shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani ya yi da zai fara aiki ranar goma sha biyu ga watan Yuni.

Wata sanarwar da kungiyar mayakan ta fitar tace shugaban kungiyar Taliban ya kuma umarci mayakan kada su yi tarukansu a wuraren da farin kaya suke zaune a lokacin hutun sallar domin al’ummar kasar su sami sukunin bukukuwan cikin kwanciyar hankali. Sai dai sun lashi takobin ci gaba da kai hare hare kan dakarun kasashen ketare da Amurka ke jagoranta a kasar.

Wannan ne karon farko tun shekara ta dubu biyu da goma sha biyu da kungiyar mayakan mai kaifin kishin Islama ta tsagaita wuta a Afhanistan, inda a halin yanzu take iko ko kuma hankoron kwace ikon rabin larduna dari hudu da bakwai na Afghanistan.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG