Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Tarayyar Turai Na Tattaunawa Kan Ficewar Burtaniya


Wani taron tattauna ficewar Birtaniya da bangarorin biyu suka yi
Wani taron tattauna ficewar Birtaniya da bangarorin biyu suka yi

Shugabannin kungiyar Tarayyar Turai sun fara wani taron koli na kwanaki biyu a Brussels yau Alhamis don tattaunawa akan duk abubuwan da suka shafi nahiyar ta su - kama daga shirin Burtaniya na fita daga kungiyar kasashen zuwa batun hanyoyin ta da komadar tattalin arzikin kasashen yankin.

Ana sa ran jawaban Firai ministar Burtaniya Theresa May a taron na kwanaki biyu zai hada da ba da tabbacin makomar mutane miliyan uku na sauran kasashen tarayyar turai da a yanzu haka suke zaune a Burtaniyyan.

Haka kuma idan aka hada da zancen makomar mutane fiye da miliyan daya ‘yan Burtaniya dake zama a wasu kasashen tarayyar turai, ana iya gane cewa wannan na daya daga cikin manyan batutuwan da dole bangarorin biyu su amince da su a wannan zaman shawarwarin da aka fara farkon makon nan.

Bayan May ta yi jawabi, a daren yau Alhamis, sauran shugabannin tarayyar za su ci gaba da taron ba tare da ita ba domin tattauna nasu bangaren shirin ballewar Burtaniyyar daga tarayyar turai.

A bara ne aka jefa kuri’ar raba gardama a Burtaniya, sakamakon da ya amince da ballewar kasar daga kungiyar.

Ana sa ran za a gama shirin a watan Maris din shekarar 2019.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG