Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinki Duniya yayi fatali da bukatar dage shari'ar da ake yiwa shugaban Kenya


Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyata da mataimakinsa William Ruto a kotun kasa da kasa dake Hague kasar Holland ko Netherlands.
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyata da mataimakinsa William Ruto a kotun kasa da kasa dake Hague kasar Holland ko Netherlands.

Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya yayi fatali da shawarar da aka gabatar cewa a jinkirta ko kuma dage shari'ar da kotun kasa da kasa ke yiwa shugaban kasar Kenya da mataimakinsa.

Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya yayi fatali da shawarar da aka gabatar cewa a jinkirta ko kuma dage shari'ar da kotun kasa da kasa ke yiwa shugaban kasar Kenya da mataimakinsa.

Jiya Juma'a da safe, kudurin da aka gabatar na dage yin shari'a da ake yiwa Uhuru Kenyatta shugaban Kenya da mataimakinsa William Ruto da tsawon watani goma sha biyu ya gaza samu kuri'ar da ake bukata da kuri'a biyu kacal.

Bakwai daga cikin wakilan kwamitin goma sha biyar ne suka jefa kuri'ar amincewa wannan mataki, yayinda takwas kuma suka jefa kuri'ar rashin amincewa.

Wannan kuduri da kasashen Afrika suka gabatar yana bukatar akalla kuri'u tara, ba tare da hawan kujeran naki daga wakilan kwamitin na dindindin su biyar ba.

Ana caji Mr. Kenyatta da mataimakinsa da aikata wa bani Adamu laifuffuka bisa zargin cewa sun shirya tarzomar bayan zabe a shekara ta budu biyu da bakwai da kuma shekara ta dubu biyu da takwas data kashe fiye da mutane dubu daya da dari daya. Dukkan shugabani biyu sun musunta zarge zargen da ake yi musu.

Kasashen da suka gabatar da kudurin dage shariar, Rwanda da Togo da kuma Morocco sun jefa kuri'ar amincewa tare da Rasha da Azerbaijan da kuma Pakistan. Amirka da Ingila da Faransa suna daga cikin kasashen da suka kauracewa jefa kuri'a akan kudurin.
XS
SM
MD
LG