Yau za a kara tsakanin Liverpool da Madrid a zagaye na biyu a wasan neman lashe kofin zakarun nahiyar turai a matakin Quarter-final.
Madrid ta lallasa Liverpool da ci 3-1 a zagayen farko a gida (Spain.)
Masu sharhi na ganin Liverpool na da jan aiki a gabanta a wasan da za a kara a zagaye na biyu duk da cewa ta yi iya bakin kokarinta a zagayen na farko.
Hakazalika, a yau ne Manchester City ta Ingila za ta gwada kaiminta da Borussia Dortmund ta kasar Jamus.
Dortmund ce za ta karbi bakuncin City a wannan wasa.
A wasan da suka kara a zagayen farko, City ta doke Dortmund da ci 2-1.
Ya ya kuke ganin wadannan wasanni za su kaya?