Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mai Yiwuwa Amurka Ta Fice Daga Yarjejeniyar Takaita Makaman Nukiliya


Alamu na nuna cewa mai yiwuwa Amurka ta fice daga yarjejeniyar takaita makaman nukiliya da ta kulla da babbar abokiyar hamayyarta Rasha.

Bisa ga dukkan alamu, gwamnatin shugaban Donald Trump na shirin ficewa daga wata yarjejeniyar da aka rattabawa hannu a shekarar 1987, ta takaita makaman nukiliya tsakaninta da Rasha.

Wannan alama ta ficewa daga yarjejeniyar ta fara bayyana ne bayan wata ganawa da mai bai wa shugaban Donald Trump shawara a harkar tsaro John Bolton ya yi da shugaba Vladimir Putin.

Shugaba Donald Trump ya zargi Rasha da karya ka’idojin da aka saka a yarjeneniyar ta makamai masu cin matsakaicin zango, wadanda ya ce har yanzu Rasha na amfani da su.

Mr. Bolton ya kira wannan matakin a mtsayin karya ka’idar a matsayin dadaddiya kuma mai zurfi.

Tsohon shugaban Tarayyar Soviet, Mikhail Gorbachev, da tsohon shugaban Amurka Ronald Reagan, ne suka rattaba hannu a yarjejeniyar makaman nukiliyar a shekarar 1987.

Yarjejeniyar dai ta hanna Amurka da Rasha kera makamai, da gwaji har ma da tara makaman masu tafiyar kimanin kilominta 500 zuwa 5,000.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG