Majalisar Wakilan Najeriya ta umarci Sufeto Janar na ‘yan sanda a kasar da kuma Mai ba Shugaba Goodluck Jonathan shawara a harkarkokin tsaro su gayyaci Tsohon Shugaban ‘yan tsageran yankin Naija Delta Mujaheed Asari Dokubo da Mai ba shugaba Jonathan shawara a kan harkokin yankin Kingsley Kuku domin su ja masu kunne dangane da kalaman da suke yi game da zaben shekara ta dubu biyu da goma sha biyar.
Masu kula da lamura suna bayyana cewa, irin wadannan kalaman suna da hatsari ga ci gaban kasa madaurinki daya.
Masu kula da lamura suna bayyana cewa, irin wadannan kalaman suna da hatsari ga ci gaban kasa madaurinki daya.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.