Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Martanin Ga Korafe Korafen Yan Jam'iyyar APC Kan Rabon Mukamai


Shugaba Mohammadu Buhari
Shugaba Mohammadu Buhari

Fadar Shugaban Nigeria, Muhammadu Buhari, ta maida murtani ga korafe-korafen da aka ce wasu ‘yan jam’iyyar APC mai mulkin kasar suna yi dangane da yadda take raba mukaman gwamnati.

Wannan ya biyo bayanda wasu manyan ‘yan siyasa na kasar suka ki karbar mukaman jakadancin da shugaba Buharin ya so ya basu a cikin makon nan. Ko a taron da aka yi tsakanin shugaba Buhari da gwamnonin kasar ance wannan korafin ya tuzgo.

A hirarshi da wakilin Muryar Amurka na Abuja Umar Faruk Musa, kakkin fadar shugaban kasar, Garba Shehu yace ai akwai wata tsohuwar yarjejeniya tsakanin shugaba Buhari da gwamnoni dake cewa kowa ya tsaya nasa gefen in dai ana maganar rabon mukamai ne.

Ga abin da Mallam Garba Shehu ke cewa:

please wait

No media source currently available

0:00 0:00:40 0:00

XS
SM
MD
LG