Yau kwana biyu da kasar Mozambique ta ayyana zaman makoki da juyayi bayan da wata muguwar guguwa mai suna Idai ta afkawa yankin na kudancin nahiyar Afrika, har daruruwan mutane suka mutu..
Jami'ai sun tabbatar da cewa adadin wadanda suka mutu a Mozambique, da Zimbabwe da kuma Malawi ya zarta 300.
Kwararru a fannin yanayi, sun yi hasashen cewa za a yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a yau Alhamis kuma yawan ruwan da yayi ambaliya na dada karuwa. Ƙungiyoyin kai agaji na can na ƙoƙarin kai kayayyakin agaji ga wadanda suka tsira kuma suke matukar bukatar kayan.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 27, 2023
An Samu Take Hakkin Dan Adam Da Dama a Jamhuriyar Nijar - Rahoto
-
Janairu 25, 2023
Ma’aikatan Kasar Nijar Sun Fara Yajin Aiki Na Wuni Biyu
-
Janairu 25, 2023
Dalilin Da Yasa Amurkawa Bakaken Fata Ke Kaura Zuwa Ghana
Facebook Forum