Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Kori Wasu Bakin Haure Daga Jihar Borno


Najeriya Ta Kori Wasu Bakin Haure Daga Jihar Borno
Najeriya Ta Kori Wasu Bakin Haure Daga Jihar Borno

Hukumomin kula da shige da ficen baki sun ce yanayin tsaro da kuma kusantowar zabe a shekara mai zuwa suka sanya su daukar wannan matakin

Najeriya ta kori wasu bakin haure kimanin 700 a wani bangare na kokarin murkushe wadanda ake zaton ‘ya’yan wata kungiyar tsagerancin addini ce.

Babban jami’in hukumar kula da shige da ficen baki a Jihar Borno, Babayo Alkali, ya fada jiya alhamis cewa bakin da aka kora ba su da cikakkun takardun zama a kasar, kuma sun fito ne daga kasashen Nijar da Kamaru da Chadi. Yace korar mutanen ta zamo dole a saboda halin tsaron da ake ciki a Jihar Borno da kuma zaben shugaban kasa dake tafe a shekara mai zuwa.

Alkali bai ambaci kungiyar nan ta Boko Haram ba, wadda aka dora ma laifin kai wasu hare-hare a cikin ‘yan watannin nan a arewacin Najeriya. Hare-haren sun hada da wadanda aka kai kan caji ofis na ‘yan sanda da kuma harbe ‘yan sandan. Akasarin wannan fitina ta wakana ne a Jihar Borno. An girka sojoji a yankin a dalilin hakan.

XS
SM
MD
LG