Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsagerun Niger Delta Sun Musanta Suna Da Hanu A Sabon Harin Bama-Bamai A Abuja


Wata mace wacce ta rasa dan'uwa a tashin Bam a Abuja,tana kuka ne a babban asibitin Asokoro dake Abuja,ranar jumma'a 31 ga watan Disemba.
Wata mace wacce ta rasa dan'uwa a tashin Bam a Abuja,tana kuka ne a babban asibitin Asokoro dake Abuja,ranar jumma'a 31 ga watan Disemba.

Tsagerun yankin Niger Delta a Nigeria, sun musanta cewar suna da hannu wajen kai harin boma-boman da suka janyo asarar rayukan akalla mutane hudu a jajiberen kirsimeti a birnin tarayyar Nigeria na Abuja.

Tsagerun yankin Niger Delta a Nigeria, sun musanta cewar suna da hannu wajen kai harin boma-boman da suka janyo asarar rayukan akalla mutane hudu a jajiberen kirsimeti a birnin tarayyar Nigeria na Abuja.

Kungiyar ‘yan tsagerun Niger Delta ta (MEND) ta musanta zargin ne a wata sanarwar da ta bayar a daren Asabar da ta gabata.

Idan an tuna, kungiyar (MEND) tace ita keda alhakin tada bom a Abuja ran bikin mulkin kan Nigeria daya ga watan Oktoba wanda ya janyo mutuwar mutum 12.

XS
SM
MD
LG