Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ONDO: ‘Yan Sanda Sun Kubutar Da Akalla Mutane 77 Ciki Har Da Yara Daga Wata Majami’a


Wasu yan sanda
Wasu yan sanda

‘Yan sanda a Najeriya sun kubutar da akalla mutane 77 da wasu fastoci suka ajiye a wani ginin cocin inda su ke jiran zuwan Yesu Almasi’u na biyu, kamar yadda hukumomi suka fadi jiya Lahadi.

Mutanen da aka ceto a daren Juma’a daga cocin da ke jihar Ondo sun hada da yara 23, wasu kuma ‘yan kasa da shekara 8. Mazauna yankin sun shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press cewa an ajiye wasu mambobin Cocin Whole Bible Believer a can tun bara.

Fastoci a cocin da ke da nisan kilomita 75 (mil 46) daga babban birnin Abuja, sun karfafa wa ’yan kungiyar gwiwa su “dakata” su jira lokacin fyaucewa, in ji kakakin ‘yan sandan Ondo, Funmilayo Odunlami.

Fastoci biyu suna tsare, koda yake masu binciken ba su sami shaidar da ke nuna cewa an “ci zarafin mambobin cocin ko tilastasu su zauna a cikin ginin ba, in ji ta.

“Mataimakin Fasto ya ce ya gaya musu abin da Ubangiji ya gaya masa; su yi biyayya ga iyayensu cikin Ubangiji,” inji Odunlami.

Najeriya kasa ce mai zurfin addini inda ake girmama shugabannin addini da yawa. Wannan dai ba shi ne karon farko da hukumomi ke bayar da rahoton kubutar da mutanen da malaman addini suke tsare da su ba, na son rai ko kuma da karfi.

Wata mata ce ta tona asiri game da yiwuwar yin garkuwa da cocin Ondo ta yi, inda ta ce ba a ba ’yarta izinin yin rajistar jarrabawarta ba, in ji mazauna yankin.

Wasu mazauna wurin sun koka da rashin jin daɗi game da cocin amma ba su san abin da ke faruwa a ciki ba.

Tunde Valentino, wanda ke zaune a kusa, ya ce "Suna gudanar da ayyuka a kowane lokaci kuma mutane ba sa yin barci lokacin da suke gudanar da shirye-shiryensu." "A ranar Talata ne wata mata ta zo tana cewa sun ki su saki 'ya'yanta guda biyu."

Lokacin da hukumomin yankin suka je wurin, wasu ’yan coci sun bijire wa masu son cetonsu kuma “sun ƙi zuwa,” suna la’antar iyayen da su ma suka zo, a cewar Valentino.

Famakinwa Lucaskakaki, shugabar wata kungiyar matasan yankin, ta ce a yayin da ake yi musu tambayoyi, mambobin cocin sun nace cewa “sun shiga cikin ginin da kansu” bayan wa’azin da ake yi a kowace Lahadi.

“Wasu daga cikinsu sun ce suna zaune ne a can tun watan Agusta; wasu kuma sun ce sun isa wurin ne tun watan Janairun bana,” inji shi.

~ AP

Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG