A yau Laraba ake sa ran Majalisar wakilan Amurka za ta kada kuri'a kan batun tura takardun hujjojin tsige shugaban Amurka Donald Trump, zuwa ga majalisar dattawan kasar, don fara zaman shari’ar da ake sa ran farawa a makon gobe.
Majalisar ta amince da takardun hujjojin ne a watan da ya gabata, amma kakakin majalisar Nancy Pelosi, ta jinkirta tura takardun yayin da 'yan Demokrat a majalisar wakilai, suka yi kokarin ganin shugabannin majalisar dattawa sun yarda a saurari bahasi daga wasu sabbin shaidu a lokacin zaman shari’ar.
Har yanzu dai ba a warware batun ba. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa Mitch McConnell, ya ki yarda da matakin kiran shaidun, kuma ya ce za a yanke wannan shawarar daga baya a yayin da ake shari’ar.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 23, 2021
Jirgin Hukumar Sama Jannatin Amurka Ya Isa Tashar Sararin Sama
-
Fabrairu 22, 2021
COVID-19 :Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kusa Rabin Miliyan A Amurka
-
Fabrairu 20, 2021
Amurka Ta sake Komawa Cikin Yarjejeniyar Sauyin Yanayi A Hukumance
-
Fabrairu 17, 2021
Texas-Dussar Kankara Ta Haifar Da Dauke Wuta A Gabashin Amurka
-
Fabrairu 14, 2021
Yadda Majalisar Dattawan Amurka Ta Wanke Trump
Facebook Forum