Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Fitar Da Jerin Sunayen Kasashen Da Ke Take Hakkin Bil Adama a Kullum


Amurka ta ce da China da Rasha masu yada tashin hankali a duniya ne, saboda yadda su ke kin kiyaye hakkin dan adam; haka ma Koriya Ta Arewa da Iran.

A rahotonta na shekara-shekara kan hakkin dan adam wanda ta fitar jiya Jumma’a, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta zargi kasashen hudu da take hakkin dan adam, ciki har da batun ‘yancin fadin albarkacin baki da batun kare tsirarun mabiya wasu addinai da kuma kananan kabilu.

Mukaddashin Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Sullivan ya fadi a babin gabatarwa na rahoton cewa kasashen hudu “su na take hakkin mutanen da ke cikin kasashensu kulluyaumin.”

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG