Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikicin Boko Haram Ya Lankwame Rayukan Mutum Dubu 11 Inji Wani Nazari

Irin hare-haren 'yan boko haram masu hallaka mutane a arewa maso gabashin Najeriya.
Irin hare-haren 'yan boko haram masu hallaka mutane a arewa maso gabashin Najeriya.

Sashen Nazarin Al’amurran Yau da Kullum na Duniya a Jami’ar John Hopkins ta nan Amurka ne ya gabatar da rahoton.

Wani sabon rahoton da ya fito yace a lalace mutanen da aka hallaka a sanadin ta’asar ‘yan Boko Haram a sashen arewa-maso-gabashin Nigeria sun kai mutane dubu goma sha daya.

Wadanan alkalumman sun bayyana ne a cikin wani nazarin da Sashen Nazarin Al’amurran Yau da Kullum na Duniya a Jami’ar John Hopkins ta nan Amurka ta gudanar bayanda ta hada hancin jimillar yawan mutanen dake rasa rayukkansu tun daga lokacinda aka faro wannan tashin hankalin a shekarar 1998.

A cikin wannan kasidar da aka wallafa a cikin jaridar Washington Post, masu nazarin sunce yau a duniyar nan, ba wata tarzoma da kai ta Boko Haram ta fuskar asarar rayukkan mutane da ake. Kasidar tace ko a cikin shekara daya kawai, daga watan Yulin 2013 da watan Yunin wannan shekarar da muke ciki, mutanen da aka kashe a tarzomar Boko Haram din tafi mutane 7,000, har ta nuna cewa ko ka hada hancin yawan mutanen da ake kashewa a yake-yaken Iraq da Afghanistan, ba zasu kai yawan wadanda ke hallaka a hannun ‘yan Boko Haram da ma’aikatan tsaron Nigeria ba, wadanda suma rahoton yace ana zarginsu da yiwa dimbin mutane kisan gilla a kokarin da suke na jan daga da ‘yan Boko Haram din.

Rahoton yace in aka hada hancin dukkan mutanen Nigeria da suka rasa rayukkansu a tashe-tashen hankulla masu alaka da addini, kabilanci, siyasa da tattallin arziki da suka faru daga 1998 zuwa yau, za’a ga cewa sun fi dubu talatin.

This item is part of
XS
SM
MD
LG