Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Robert Mugabe Yayi Murabus Daga Karshe


Bayan kwashe shekaru talatin da bakwai a karkashin mulkin Robert Mugabe, kasar Zimbabwe zata auri wani sabon shugaban.

Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe yayi maraous bayan shafe shekaru talatin da bakwai yana mulkin kasar.

Yin murabus din nasa ya biyo bayan matsin labar da Sojojin kasar da kuma jam’iyyar sa ta ZANU PF suka yi.

Kakakin majalisar kasar ta Zimbabwe, Jacob Mudenda, ya karantawa majalisar wasika da tsohon shugaba Robert Mugabe ya rubuta, inda ya ce “Ni Robert Gabriel Mugabe, a bisa sashe na 96, na kundin tsarin mulkin Zimbabwe na sauka daga mulki batare da bata lokaci ba.”

Ba a sami tabbacin wasikar daga ofishin Mugabe ba. Amma tuni jama’ar gari suka cigaba da nuna murna inda suka bi tituna da kade kade da raye raye.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG