WASHINGTON, D.C —
Daga yau Jumma’a Kerry zai fara ziyarar ta sa ta tsawon kwanaki biyu a birnin Addis Ababa, inda a cewar Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, zai gana da manyan jami’an gwamnatin kasar Habasha don tattaunawa kan batutuwan da su ka shafi kasashen biyu.
Gobe Asabar zai bi sahun shugabannin kasashen Afirka da sauran manyan baki daga wasu kasashen a babban taron kungiyar Tarayyar Afirka, inda za'a yi bikin cika shekaru 50 da kafa kungiyar Tarayyar Afirka din, wadda a baya ake kiranta Kungiyar Hadin Kan Afirka (OAU).
Ana kyautata zaton ziyarar ta Kerry za ta hada da tattaunawa kan fafatukar da ake yi da masu tsattsauran ra’ayin Islama a kasashe irin su Mali da kuma arewacin Nijeriya.
Gobe Asabar zai bi sahun shugabannin kasashen Afirka da sauran manyan baki daga wasu kasashen a babban taron kungiyar Tarayyar Afirka, inda za'a yi bikin cika shekaru 50 da kafa kungiyar Tarayyar Afirka din, wadda a baya ake kiranta Kungiyar Hadin Kan Afirka (OAU).
Ana kyautata zaton ziyarar ta Kerry za ta hada da tattaunawa kan fafatukar da ake yi da masu tsattsauran ra’ayin Islama a kasashe irin su Mali da kuma arewacin Nijeriya.