Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sakatare Kerry Ya Soke Ganawa da Shugabannin Falasdinu


Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry
Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry

Sabili da shugabannin Falasdinun sun yi gaban kansu sun rubutawa Majalisar Dinkin Duniya suna neman tasu kasar sakataren harkokin wajen Amurka ya soke ganawa da shugabannin

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya soke shirin ganawa da shugaban Palasdinawa Mahmud Abbas, da da aka shirya zasu yi yau laraba a birnin Ramalla dake yammacin kogin Jordan.

Kerry ya soke ziyarar bayanda shugaba Abbas yace hukumomin Falasdinu ba tareda wani bata lokci ba zasu ci gaba da daukan matakai na neman yardar Majalisar Dinkin Duniya (MDD) a matsayin kasa, har tuni yankin ya tura bukatar neman zama wakili a hukumomin MDD 15.

Nan da nan dai, Isra’ila bata ce kome ba akan wannan mataki, sai dai jami’an kasar jiya talata sun sake gabatar da takardun aikin gina gidajen ‘yan share wuri zauna fiyeda dari bakwai a gabashin birnin kudus.
XS
SM
MD
LG