Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shawo Kan Kalubalen Tattalin Arzikin Duniya


Shugabar Asusun Lamuni na Duniya (IMF), Christine Lagarde
Shugabar Asusun Lamuni na Duniya (IMF), Christine Lagarde

Shugabar Asusun Lamuni na Duniya (IMF), Christine Lagarde, ta fadi yau Talata cewa ya kamata duniya ta hada kai don shawo kan kalubalolin tattalin arziki, ciki har da tafiyar hawainiya da tattalin arziki ke yi, da faduwar farashin kaya da kuma tsuke bakin aljuhun da gwamnatoci da dama ka yi nan gaba.

Da ta ke jawabi a Frankfurt, kasar Jamus, Lagarde ta ce, "tattalin arziki ya yi ta tafiyar hawainiya na lokaci mai tsawo," ta yadda mutane da dama ba su amfana, da kuma kafa tushen "matsalolin zamantakewa da siyasa a kasashe da dama."

Ta kuma zayyana kalubalolin da za a fuskanta a kasashen da su ka ci gaba, ciki har da karfin da dala za ta yi har ta jinkirta bunkasar tattalin arziki a Amurka, da jinkiri wajen saka jari da kuma rashin ayyukan yi a kasashen da ke amfani da takardar kudin Euro, da kuma tangal-tangal da tsadar kaya da za a fuskanta a kasar Japan.

To amma Lagarde ta kuma zayyana wasu kasashen da ta ce fa'ida na nan tafe. Kasar Indiya, in ji ta, na da karfin cigaba da mikewa da kuma samun karin kudaden shiga. A yankin kudancin Asiya kuwa, kasashe irinsu Indonesia, da Malaysia da Philippines, da Thailand da Vietnam na "kokari," a cewar Lagarde.

XS
SM
MD
LG