Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Goodluck Jonathan Na Najeriya Ya Sauke Ministoci 9 Daga Mukamansu


Shugaba Goodluck Jonathan ya halarci Taron Koli Na Tattalin Arzikin Najeriya (NESG) a Abuja ranar 3 ga watan Satumba.
Shugaba Goodluck Jonathan ya halarci Taron Koli Na Tattalin Arzikin Najeriya (NESG) a Abuja ranar 3 ga watan Satumba.

Wannan lamari ya faru a lokacin taro na mako-mako da Majalisar Zartaswa ta kasa tayi yau Laraba.

Wadanda wannan lamari ya shafi Hajiya Hadiza Mailafiya mai kula da Ma’akatar Muhalli, da Ruqayat Rufai ta Ma’aikatar Ilimi, da Zainab Kunchi mai kula da sha’anin Ma’aikatar Lantarki, da Bukar Tijani Ministan Cikin Gida akan harkokin sha’anin Noma, Shamsudeen Usman mai kula da Tsare-tsare na Kasa, da Ministan kula da sha’anin Kimiyya Ita Okon da Minister mai kula da Ma’aikatar Harkokin waje Olugbenga Ashiru, da Ama Pepple Mai kula da Ma’aikatar Gidaje, da Ministan kula da Tsaro na cikin gida, Olushola Obada.

Gwamnatin bata bada wata hujja ba akan dalilin da yasa Shugaban, dan jam’iyyar PDP ya sallami wadannan mutane ba, amma masu hasashe na gani an yi haka ne saboda ministocin suna da alaqa kai tsaye, ko ta gefe da gwamnonin nan su 8 da suka bijire wa gwamnati.

Akwai wasu ministoci ma da aka ce an samu korafe-korafe daga jihohinsu dake cewa basa kula da aiki. Wannan ma na daga cikin dalilan da ake tunanin sun saka Shugaba Goodluck ya sallami wadannan ministoci.

A halin yanzu dai, jam’iyyar Shugaba Goodluck Jonathan ta PDP na fama da matsalolin cikin gida, inda wasu gwamnoni da ‘ya’yan jam’iyyar suka balle suka bar shugabancin jam’iyyar karkashin Bamanga Tukur, suka koma wani sabon PDP karkashin shugabancin Kawu Baraje.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:05 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG