Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Faransa Ya Yi Allah Wadai Da Harin Nijer


Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi Allah wadai da harin da wata kungiyar ‘yan bindiga ta kai a Nijer, da ya rutsa da wasu ma’aikatan agaji na Faransa kana ya kashe akalla mutum takwas ciki har da mai musu rakiya da direban su.

Harin ya faru ne a wajen babban birnin kasar Yamai, a wani gandun namun daji da ya yi fice ga masu yawon bude ido. Wannan babbar kalubala ce ga Nijer, babbar abokiyar Amurka da sauran masu yaki da ayyukan ta’addanci a yankin Sahel.

An hakikanta cewa, wannan ne harin farko da aka kai a kan ‘yan kasashen yammacin duniya a wannan yakin na Nijer,da ya kasance shahararren dandalin yawon shakatawa mai yawan rakumar dawa a kasar dake Afrika ta Yamma.

Da yake tattaunawa da Muryar Amurka a Dakar, Gilles Yabi, shugaban wata kungiyar mai suna WAHTI, dake daukar kanta wacce ta kware a harkokin al’ummar Afrika ta Yamma, ya ce wannan harin a yanki mai fama da rikici bai zo da mamaki ba, kasancewa an shafe shekaru ana fama da matsalar tsaro a kasashen yankin Sahel.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG