Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Nijer Ya Jaddada Kudirinsa Na Magance Matsalar Cin Hanci A Kasar


Shugaban kasar Nijer ya jaddada aniyar karfafa matakan yaki da cin hanci da karbar rashawa ta yadda za a soma hukunta wadanda aka kama da hannu a irin wannan haramtacciyar dabi’a dake zama ruwan dare a Nijer kamar sauran kasashen Afrika.

Mohamed Bazoum ya bukaci ‘yan kasar su ba shi lokaci kadan domin zartar da wannan mahimmin kudiri na kwatowa kasa hakkokinta daga hannun barayin biro kamar yadda ya bayyana wa shugaban sashen Hausa Aliyu Mustapha Sokoto.

Shugaban Nijer yace babu shakka kasashen Afrika na fama da wannan matsala ta cin hanci matsalar da ya kudiri aniyar magancewa a Nijer.

Bazoum Mohamed yace ba a fuskantar cin hanci a fannin ma’adanan karkashin kasa sakamakon matakan dake gudanar da wannan fanni amma matsalar ta shafi akasarin fannoni daga jami’an tsaro zuwa fannin ilimi, lafiya, haraji. da dai sauransu.

Saurari cikakken rahoton a cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00

Babban Kalubalen Da Na Fuskanta A Watanni 7 – Shugaba Bazoum

Babban Kalubalen Da Na Fuskanta A Watanni 7 – Shugaba Bazoum
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:14 0:00

Nijar Na Bukatar Amfani Da Kudin Bai-Daya Da Najeriya – Shugaba Bazoum

Nijar Na Bukatar Amfani Da Kudin Bai-Daya Da Najeriya – Shugaba Bazoum
please wait

No media source currently available

0:00 0:08:37 0:00

Juyin Mulki A Guinea Bai Zo Da Mamaki Ba – Shugaba Bazoum

Juyin Mulki A Guinea Bai Zo Da Mamaki Ba – Shugaba Bazoum
please wait

No media source currently available

0:00 0:05:42 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG