Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sudan ta Kudu: Jakada Ya Ja Hankalin Amurka Kan Shirin Janye Tallafi


Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir
Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir

Jakadan kasar Sudan ta Kudu a Amurka, Gordon Buay, ya yi kira ga gwamnatin Amurka da ta sake tunani kan janye taimakon da take ba kasarsa saboda acewarsa, yin hakan zai shafi shirin zaman lafiya a kasarsa.

Wani babban jami’in diplomasiyar Sudan ta Kudu a Amurka ya yi kira ga Amurka da ta sake tunani kan shirin janye taimako da take bai wa Sudan ta Kudu.

A cewar Gordon Buay, hakan wani koma baya ne ga shirin samun zaman lafiyar kasar.

Jakada Buay, babban jakadan Sudan ta Kudu a Washington, ya fada cewa sanarwar da fadar White House ta fitar a shekaranjiya Talata da kakkausar kalamai a kan Sudan ta Kudu ka iya yin mummunar tasiri.


Ya kara da cewa wannan mataki zai aike da sakon da zai haifar da rashin fahimta ga 'yan tawayen kasar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG