Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sudan ta Kudu ta yi sabon mataimakin shugaban kasa


Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir.
Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir.

hugaban ‘yantattar sabuwar kasar Sudan ta Kudu ya zabi mataimakin shugaban kasa ya kuma kafa gwamnatin rikon kwarya. A dokar da ya kafa jiya Lahadi, shugaba Salva Kiir ya zabi Reik Machar a matsayin mataimakinshi.

Shugaban ‘yantattar sabuwar kasar Sudan ta Kudu ya zabi mataimakin shugaban kasa ya kuma kafa gwamnatin rikon kwarya. A dokar da ya kafa jiya Lahadi, shugaba Salva Kiir ya zabi Reik Machar a matsayin mataimakinshi. Machar ya rike wannan mukamin a tsohuwar gwamnatin yankin kudancin Sudan. An rantsar da shi yau Litinin. A wata doka dabam, shugaba Kiir ya zabi ‘yan majalisa wadanda sanarwar da gwamnati ta bayyana a matsayin ministocin wucin gadi. An sanar da Nhial Deng Nhial a matsayin ministan harkokin kasashen ketare, yayinda aka ba Pagan Amum ministan aiwatar da yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya ta shekara ta dubu biyu da biyar da ta kawo karshen yakin basasa tsakanin arewaci da kudancin Sudan, da ake kira CPA. Sabanin ra’ayi dangane da yarjejeniyar ya kara sa dangantaka tayi tsami tsakanin Sudan da kuma Sudan ta Kudu, ko da yake gwamnatin Khartoum ta amince da diyaucin Sudan ta Kudu. A cikin hirar da aka yi da shi jiya Lahadi, shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya bayyana cewa, za a kai ruwa rana a kan yankin Abyei mai arzikin man fetir idan ta kama. Sai dai ya shaidawa tashar BBC cewa, ya yi na’am da tura dakarun wanzar da zaman lafiya na kasar Habasha wadanda suke kokarin kiyaye zaman lafiya a yankin dake fama da tashin tashina.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG