Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tabarbarewar Ilimi a Nijeriya


Dalibai a makaranta.
Dalibai a makaranta.

Yara da dama basu zuwa makaranta, saboda firgicin.

Kasancewar yau ne ranar yakin da jahilci ta duniya, shugaban kungiyar wayar da kan matasa, a wannan karnin Muhammad Auwal, ya nuna rashin gamsuwarsa da yanda ilimi ke tabarbarewa a Najeriya.

Wanda yace kungiyar Boko Haram ta taka rawa wajen koma bayan ilimi a arewacin Najeriya, inda yara da dama basu zuwa makaranta, saboda firgicin.

Yace sakamakon jarabawar shiga makarantar gaba da sakandare, na bana yanuna rashin kokarin dalibai da kuma halin ko oho da suke nunawa wajen fahimtar karatu, inda kashi talatin cikin dari ne kawai suka ci jarabawa.

Muhammad Auwal yace ba’a kulawa da malamai yanda yakamata, yayi tir da yanda da yawan jami’an gwamnati, basu kai ‘yayan su a makarantun gwamnati.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:22 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG