Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Sasanta Rikicin Afghanistan a Islamabad


Taron Sasanta Rikicin Kasar Afghanistan
Taron Sasanta Rikicin Kasar Afghanistan

A yau Asabar, ana sa ran wakilai daga kasashen Amurka da China da Afghanistan da kuma Pakistan, za su amince da wani shirin zaman lafiya da ake kokarin shiryawa tsakanin gwamnatin Afghanistan da kungiyar Taliban a birnin Islamabad.

Wakilan suna kokari ne su shata wata hanya da za ta samar da zaman lafiya mai dorewa, sannan su yi nazari kan wani reshen kungiyar ta Taliban da ya bangare, wanda ya ke adawa da zaman sasantawar tare da ci gaba da kai hare-hare.

A baya, wakilan sun yi makamancin wannan zama har sau biyu a birnin na Islamabad da kuma Kabul, sai dai babu wata matsaya da aka cimma a wadannan taruka.

Mai baiwa Firai ministan Pakistan shawara kan harkokin waje, Sartaj Aziz, ya ce yana da kwarin gwiwar za a sami mafita a taron na yau.

Wadannan kasashe dai na kokari su ga yadda za su rarrashi kungiyar ta Taliban ta hau teburin tattaunawa.

XS
SM
MD
LG