Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tashin Hankalin Janhuriyar Afirka ta Tsakiya Ya Rutsa da Wasu 'Yan Nijar


Sojojin kasar Faransa kenan ke sintiri a birnin Bangui
Sojojin kasar Faransa kenan ke sintiri a birnin Bangui

Wasu 'yan Janhuriyar Nijar sun sami kansu cikin tsaka mai wuya dangane da rikicin kabilanci da addinin da ke faruwa a Janhuriyar Afirka ta Tsakiya

Yakin da ake yi a Janhuriyar Afirka ta Tsakiya ya rutsa da daruruwan 'yan Nijar da sauran 'yan wasu kasashen Afirka da ke zama a Bangui babban birnin kasar da kuma wasu biranen kasar.

Wani mazaunin birnin Bangui mai suna Nuhu Abubakar ya shaida wa wakilinmu a Janhuriyar Nijar Abdullahi Mammane Ahmadu cewa rikicin kabilanci da addinin ya sa Hausawa da Fulani da Larabawa sun taru wuri guda saboda kar wani ya abko masu. Malam Nuhu ya ce shekaran jiya an baza sojojin kasar to amma tunda sojojin Faransa da na "Alliance Farancaise" su ka iso sai sojojin kasar su ka kau.

Shi kuwa wani dan rajin kare hakkin dan adam mai suna Mustafa Kadi kira ya yi ga gwamnatin Janhuriyar Nijar da Majalisar Dinkin Duniya da su kai dauki don ceto mutanen da yakin ya rutsa da su - musamman ma wadanda ba hannunsu ciki.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:30 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG