Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Zai Halarci Bikin Rantsar Da Mahamat Deby A Chadi


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu

A ranar Alhamis 23 ga watan Mayu nan ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa birnin N’Djamena na Jamhuriyar Chadi domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Idriss Mahamat Deby Itno.

WASHINGTON, D. C. - Bikin rantsar da shi ya biyo bayan ayyana shugaba Deby a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar a farkon watan Mayu da kotun tsarin mulkin kasar ta Chadi ta tabbatar.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya fitar, wasu manyan jami’an gwamnati ne za su raka shugaba Tinubu kuma zai dawo bayan kammala bikin.

Deby, shugaban mulkin sojan Chadi, ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar 6 ga watan Mayu ne, da kashi 61 na kuri'un da aka kada, a cewar sakamakon karshe da aka sanar.

Sai dai babban abokin hamayyarsa Succes na kalubalantar sakamakon zaben.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG