Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump Na Jefa Ayar Tambaya Kan Yanayin Tunanin Abokin Adawarsa


Shugaban Amurka Donald Trump na jefa ayar tambaya kan yanayin hankali da tunanin abokin karawarsa a zaben watan Nuwamba, wato tsohon mataimakin shugaban Amurka Joe Biden, bayan haka ya na nuna cewa bai cancanta ya zama shugaban kasa ba.

A wata hira da aka yi da shi a wani shiri na musamman na ranar Lahadi a gidan talabijin din Fox News inda Trump ya caccaki tsohon mataimakin Shugaban, ya nuna cewa Biden bai iya hada jumla biyi a bayaninsa.

Zasu gabatar da shi a wuri. Zai tashi ya je, ya maimaita abu, za su yi masa tambayoyi. Zai yi karatu daga na’urar nuna karatu daga nan ya sake labewa, a cewar Trump. Ku fada min ko Amurkawa zasu so su samu irin wannan mutumin a zamanin da mu ke fuskantar matsaloli, wasu kasashen na neman hanyar yi mana illa.

Kwamitin yakin neman zaben Trump ya saki wasu tallace-tallace masu jefa ayar tambaya a kan ko yanayin hankalin Biden mai shekaru 77, wanda zai zama shugaban Amurka wanda ya fi yawan shekaru idan ya yi nasara a zaben ranar uku ga watan Nuwamba kana aka rantsar da shi a watan Janairu mai zuwa, ya fara gushewa ko a'a. A halin yanzu dai Trump mai shekaru 74 shi ne shugaba mafi yawan shekaru a Amurka.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG