Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

TSARO: An Kashe Mutane 16 A Rikicin Kabilanci A Jihar Filato


Wasu yan bindiga
Wasu yan bindiga

Mutane 16 ne aka kashe a wasu hare-hare biyu da aka kai a arewa maso tsakiyar Najeriya a yankin da ke fama da rikicin kabilanci, in ji rundunar sojoji.

Rikici ya barke tsakanin makiyaya da manoma a jihar Filato, wanda ke kan iyaka tsakanin arewacin kasar inda galibi Musulmai ne da kuma kudancin Najeriya wadanda galibinsu mabiya addinin Kirista ne.

A wani sabon tashin hankalin da ya barke a ranar Talatar da ta gabata, wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan kungiyar manoman yankin a gundumar Riyom, yayin da wasu mutane 10 suka mutu a wani hari da aka kai a yankin Mangu, in ji kakakin rundunar.

Wasu da aka kashe
Wasu da aka kashe

"An rasa rayuka shida a Riyom," Manjo Ishaku Takwa ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa na AFP a ranar Laraba.

"An kuma sake kai wani hari a wasu al'ummomi a Mangu inda mutane 10 suka mutu."

Dan Majalisar Jihar Filato mai wakiltar Mangu ta Kudu, Bala Fwangje, ya ce an kashe mutane 14 a yankin.

“Mun ji an kashe mutane kusan 14, an lalata gidaje, an kuma kona dukiyoyi amma har yanzu ban samu cikakken bayani ba,” inji shi.

'Yan bindiga sun kona gidaje a Jos
'Yan bindiga sun kona gidaje a Jos

Tun a watan Mayu, kusan mutane 200 ne aka kashe a rikicin da ya barke tsakanin al’ummar kabilar Berom, wadanda galibi Kiristoci ne, da kuma al’ummar Musulmi Fulani masu kiwo a yankunan Riyom, Barikin Ladi da Mangu na Filato.

Ba a dai san ko me ya jawo hare-haren na baya-bayan nan a Filato ba, amma kashe-kashen ramuwar gaya da ake yi tsakanin makiyaya da manoma yakan bazu har zuwa kauyukan da wasu gungun ‘yan bindiga dauke da muggan makamai ke yi wa jama’ar gari fashi da garkuwa da mutane da kuma kashe su.

Rikicin Filato na daya daga cikin kalubalen tsaro da shugaba Bola Tinubu ke fuskanta, wanda ya karbi ragamar mulkin kasar mafi yawan al'umma a Afirka a karshen watan Mayu.

XS
SM
MD
LG