Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Dalibi Ya Harbe Mutane 19 a Rasha


Wani dalibi mai shekaru 18 ya harbe ya kashe mutane 19 kana ya jikata sama da wasu hamsin a wata kwalejin kere kere a Crimea.

‘Yan sanda sun ce Vladislay Roslyakov ne ya yi harbin, dalibin ajin karshe a kwalejin dake birnin Black Sea a yankin Kerch na Crimea.

Masu bincike da darekatan kwalejin sun fada cewa, bayan wata fashewa, sai wani dan bindiga ya shiga ginin makarantar ya fara harbin kan mai uwa ba wabi a Kwalejin kere kere a yankin Kerch.

Dmitry Peskov, shine mai magana da yawun shugaban Rasha, yace Vladmir Putin ya bada umarnin gudanar da binciken kwakwaf a kan wannan batu kana ya aike da ta’aziyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG