Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani madugun kungiyar tsagera Tom Ateke ya mika sansanoni takwas ga jami'an tsaro


Mayakan Tom Ateke a daya daga cikin sansanoninsu
Mayakan Tom Ateke a daya daga cikin sansanoninsu

Wani madugun kungiyar tsagera a yankin Niger Delta Tom Ateke ya mika sansanoni takwas ga jami'an tsaro.

Rundunar sojojin Najeriya ta ce wani madugun tsagera a yankin Niger Delta mai arzikin man fetur ya mika sansanoni guda 8 ga hukumomi. Ateke Tom ya mika wadannan sansanoni dake cikin Jihar Rivers ne a cikin ‘yan kwanakin da suka shige. Ateke Tom yana daga cikin shugabannin tsageran da suka yi na’am da ahuwar da gwamnati ta yi musu da nufin wanzar da kwanciyar hankali a yankin na Niger Delta mai fama da fitina. Hare-hare da sace-sacen mutane da ake yi a yankin, musamman a kan masana’antar, sun rage yawan man da Najeriya ke hakowa da kudaden shugar da take samu a cijkin ‘yan shekarun nan. Rundunar sojoji tana ci gaba da kai farmaki a kan tsageran da suka ki yarda da shirin ahuwar. A cikin wannan watan, sojoji sun kai farmaki a kan wasu sansanoni uku na wani madugun tsagera da ake kira John Togo. Shaidu da kuma kungiyoyin kare hakkin bil Adama sun ce an kashe fararen hula da dama a fadan. Togo dai ya tsere ba a kama shi ba. A watan da ya shige ma, sojoji sun kai farmaki a kan sansanonin wani madugun tsagera mai suna Obese inda suka kwato mutane 19 da aka yi garkuwa da su.

XS
SM
MD
LG