Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Adawar Hong Kong Sun Yi Zaben Fidda Gwani Na 'Yan Rajin Dimokradiyya


Kusan mutum 600,000 suka kada kuri’unsu a wani zaben fidda gwani da aka yi ba tare da amincewar hukumomin Hong Kong ba, domin tantance shugabannin masu rajin kare dimokradiyyar da za su tsaya takara a watan Satumba.

Bangaren ‘yan adawa a yankin na Hong Kong ne ya shirya wannan zabe, wanda ake gani ya saba wa sabuwar dokar nan mai cike da takaddama da hukumomin Beijing suka kafa a yankin.

A dai watan Satumba ake shirin yin zaben ‘yan majalisar dokoki a Hong Kong.

Daruruwan dubban mutane ne suka fita wannan zabe a karshen makon da ya gabata, duk da cewa hukumomi sun yi gargadin hakan zai saba wa sabuwar dokar tsaro da China ta saka wa yankin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG